1 Na yi kuka ga Allah don taimako;
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji;
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi;
4 ka hana idanuna rufewa;
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce,
6 na tuna da waƙoƙina da dare.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan,
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji;
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne.
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai;
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka,
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah,
17 Gizagizai sun sauko da ruwa,
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa,
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku,
20 Ka bi da mutanenka kamar garke