1 Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila,
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi;
3 Gama na yi kishin masu girman kai
4 Ba sa yin wata fama;
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha;
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya;
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa;
9 Bakunansu na cewa sama na su ne,
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani?
12 Ga yadda mugaye suke,
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta;
14 Dukan yini na sha annoba;
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,”
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan,
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah;
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi;
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya,
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka,
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci
22 na zama marar azanci da jahili;
23 Duk da haka kullum ina tare da kai;
24 Ka bishe ni da shawararka,
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba?
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana,
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka;
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah.