1 Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona;
2 Ya kai wanda yake jin addu’a
3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu,
4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa
5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci,
6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka,
7 wanda ya kwantar da rurin tekuna,
8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka;
9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa;
10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta;
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka,
12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba;
13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna