1 Ka ji kukata, ya Allah;
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka,
3 Gama kai ne mafakata,
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah;
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki,
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada;
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka