1 Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma;
3 Raina yana cikin wahala.
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni;
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu.
6 Na gaji tiƙis daga nishi.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki;
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta,
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa;
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya;