1 Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji,
2 Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni,
3 gama ƙaunarka kullum tana a gabana,
4 Ba na zama tare da masu ruɗu,
5 na ƙi jinin taron masu aikata mugunta
6 Na wanke hannuwana cikin rashin laifi,
7 ina shelar yabonka da ƙarfi
8 Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji,
9 Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi
10 waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu,
11 Amma na yi rayuwa marar zargi;
12 Ƙafafuna suna tsaye daram;