1 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye;
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji;
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye;
5 Masu girman kai sun sa mini tarko;
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.”
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi,
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji;
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu;
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar;
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka