1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi;
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan,
3 su da ya tattara daga ƙasashe,
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada,
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa,
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya;
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa
18 Ba su so su ga abinci ba
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji,
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa;
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu;
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit;
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta,
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane
33 Ya mai da koguna suka zama hamada,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani,
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa
36 a can ya kai mayunwata su yi zama,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru,
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa