1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali,
4 don sa marar azanci yă yi hankali,
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu,
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai,
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi,
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka,
11 In suka ce, “Zo mu tafi;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari,
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri,
14 ka haɗa kai da mu,
15 ɗana, kada ka tafi tare da su,
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi,
17 Ba shi da amfani a kafa tarko
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko;
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau;
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi,
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu,
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci?
23 Da a ce kun saurari tsawatata,
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira
25 da yake kun ƙi dukan shawarata
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri,
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba;
29 Da yake sun ƙi sani
30 da yake ba su karɓi shawarata ba
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su,
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya