1 Ni ne mutumin da ya ga azaba
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni
6 Ya sa na zauna a cikin duhu
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba;
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako,
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu;
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira,
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni
12 Ya ja kwarinsa
13 Ya harbi zuciyata
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka;
15 Ya cika ni da kayan ɗaci
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa;
17 An hana ni salama;
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri,
20 Na tuna su sosai,
21 Duk da haka na tuna da wannan
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba;
23 Sababbi ne kowace safiya;
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa;
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa,
26 yana da kyau ka jira shiru
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai,
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi,
31 Gama Ubangiji ba ya
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai,
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala
34 Bai yarda a tattake
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta,
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu;
44 Ka rufe kanka da gajimare
45 Ka mai da mu tarkace da juji
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana
47 Muna cika da tsoro,
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye,
50 Har sai in Ubangiji ya duba
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki
52 Maƙiyana suna farauta ta
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami
54 ruwaye suka rufe kaina,
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji,
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka,
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana;
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba.
60 Ka ga zurfin ramakonsu,
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai
63 Dube su! A zaune ko a tsaye,
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji,
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu,
66 Ka fafare su cikin fushi