1 “Kaiton ’ya’ya masu tayarwa,”
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya,
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan
5 kowa zai sha kunya
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa,
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne.
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo,
9 Waɗannan mutane masu tawaye, ’ya’ya masu ruɗu,
10 Sukan ce wa masu gani,
11 Ku bar wannan hanya,
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa,
13 wannan zunubi zai zama muku
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu,
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa,
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’
17 Dubu za su gudu
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri;
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa,
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu
29 Za ku kuma rera
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu
33 An riga an shirya wurin ƙonawa;