1 Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai;
2 Al’ummai za su ɗauke su
3 A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a.
5 Ubangiji ya karye sandar mugaye,
6 wanda cikin fushi ya kashe mutane
7 Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama;
8 Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon
9 Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya
10 Duk za su amsa,
11 An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari,
12 Yaya aka yi ka fāɗo daga sama
13 Ka yi tunani a ranka ka ce,
14 Zan haura can bisa gizagizai;
15 Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari,
16 Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido,
17 mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada,
18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace,
19 Amma an jefar da kabarinka
20 ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba,
21 A shirya wuri don a yayyanka ’ya’yansa maza
22 “Zan yi gāba da su,”
23 “Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi
24 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse,
25 Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata;
26 Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya;
27 Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi?
28 Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa,
30 Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo,
31 Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni!
32 Wace amsa ce za a bayar