1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka;
2 Ka juye kunnenka gare ni,
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata,
4 Ka ’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini,
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna;
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza;
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka,
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa;
10 Baƙin ciki ya rufe raina
11 Saboda dukan abokan gābana,
12 An manta da ni sai ka ce na mutu;
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa;
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji;
15 Lokutana suna a hannuwanka;
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka;
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji,
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu,
19 Alherinka da girma yake,
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji,
22 Cikin tsorona na ce,
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa!
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa,