1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu;
2 An ba wa baƙi gādonmu,
3 Mun zama marayu marasa ubanni,
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha;
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu;
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya
7 Kakanninmu sun yi zunubi
8 Bayi suna mulki a kanmu,
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu,
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona,
12 An rataye ’ya’yan sarakuna da hannuwansu;
13 Samari suna faman yin niƙa;
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin,
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu;
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi;
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai,
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada;
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo;
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya