1 “ ‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa,
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce?
6 Na saurara sosai,
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma
8 “ ‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima,
9 Za a kunyatar da masu hikima;
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu
11 Sukan ɗaura mikin mutanena
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa?
13 “ ‘Zan ƙwace girbinsu,
14 Me ya sa muke zama a nan?
15 Mun sa zuciya ga salama
16 Daga Dan ana jin
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku,
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki,
19 Ka saurari kukan mutanena
20 “Girbi ya wuce,
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan;
22 Ba magani ne a Gileyad?