1 Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
2 “Ba amfani! Ba amfani!”
3 Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar
4 Zamanai sukan zo zamanai su wuce,
5 Rana takan fito rana ta kuma fāɗi,
6 Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa;
7 Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku,
8 Dukan abubuwa suna kawo gajiya,
9 Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance,
10 Akwai wani abin da za a ce,
11 Ba a tunawa da mutanen dā,
12 Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
13 Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
14 Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
15 Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba;
16 Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
17 Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
18 Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki;