1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona,
2 Ku je Kalne ku dube ta;
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta;
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta,
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni,
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu?
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce,