Jeremias 14

HAUSA

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,

2 “Yahuda tana makoki

3 Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa

4 Ƙasa ta tsattsage

5 Har barewa a kurmi ma

6 Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai

7 Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu,

8 Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila,

9 Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato,

10 Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane,

11 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.

12 Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”

13 Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’ ”

14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.

15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.

16 Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko ’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.

17 “Ka yi musu wannan magana,

18 In na shiga cikin ƙasar,

19 Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan?

20 Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu

21 Saboda sunanka kada ka ƙi mu;

22 Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama?

Ler em outra tradução

Comparar lado a lado